HomeLabarai’Yan bindiga sun kashe mutum 9 ’yan gida daya a Filato

’Yan bindiga sun kashe mutum 9 ’yan gida daya a Filato

Date:

Related stories

Abba gida-gida ya lashe zaben gwamnan Kano

Hukumar Zabe ta Kasa, INEC ta sanar da cewa...

INEC na neman ta ce zaben gwamnan Kano ‘Inconclusive’ ne — Kwankwaso

Dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar NNPP, sanata Rabiu...

Zaben gwamnan Kano: Ratar kuri’ar da ke tsakanin NNPP da APC

Bayan bayyana sakamakon kananan hukumomi 44 na zaben gwamnan...

Jami’in tattara sakamakon zabe ya yanke jiki ya fadi a hedikwatar INEC a Kano

Jami’in tattara sakamakon zabe, Farfesa Muhammad Yushau na karamar...

Sakamakon zaben gwamnonin jihohin Najeriya

Wannan shafin zai rika kawo muku kammalallen sakamakon zaben...

’Yan bindiga sun kashe wasu mutum tara ’yan gida daya a kauyen Maikatako da ke Karamar Hukumar Bokkos ta Jihar Filato.

Kakakin rundunar ’yan sandan Jihar Filato, Mista Alfred Alabo, ya tabbatar da faruwar lamarin yayin taron manema labarai a ranar Laraba.

Alabo ya ce ’yan bindigar da suka afka wa kauyen a daren Talata kai tsaye suka shiga harbi kan mai uwa da wabi.

Kakakin ’yan sandan wanda ya ce tuni bincike ya kankama kan faruwar lamarin, ya kuma sha alwashin yi wa manema labarai karin haske a nan gaba kadan.

Wani mazaunin kauyen da zanta da Kamfanin Dillancin Labarai na Najeriya NAN, ya ce zuwa yanzu dai sun tsinto gawarwakin mutum 18 kuma suna ci gaba da lalube.

A cewarsa, akwai fargaba a tsakanin al’ummar duk da kasancewar jam’ian tsaro da suka hada da ’yan sanda da sojoji da ke ci gaba da sintiri.

Subscribe

- Never miss a story with notifications

- Gain full access to our premium content

- Browse free from up to 5 devices at once

Latest stories