Dan takarar shugaban kasa a jamâiyyar PDP, Atiku Abubakar, ya bayyana cewa ya goge sakon da ya wallafa a shafinsa na Twitter inda ya yi Allah wadai da kisan da aka yi wa Deborah Samuel, daliba da aka zarge ta da laifin cin zarafi, saboda an yada ta ne ba tare da amincewar sa ba.
Deborah, wata daliba Kirista mai mataki 200 a Kwalejin Ilimi ta Shehu Shagari da ke Sokoto, wasu dalibai ne suka kasheta a watan Mayu bisa zargin zagin Annabi Muhammad.
A yayin taron mutanen gidan Talabijin na Channels a ranar Lahadi, an tambayi Atiku dalilin da ya sa ya goge sakon Twitter inda ya yi Allah-wadai da lamarin.
A martanin da Atiku ya mayar, ya ce, âNa nemi a goge sakon Twitter din ne saboda a kaâida na amince da kowane tweet din, kuma tunda ban amince da tweet din ba, sai na ce su goge shi. Idan ka karanta bayanina na baya kan wannan kisan, na yi Allah wadai da shi.â
Bayan kashe Deborah, wani sakon da Atiku ya wallafa a shafinsa na Twitter ya ce, “Ba za a iya samun hujjar irin wannan mugun kisa ba. An kashe Deborah Yakubu kuma duk wadanda suka kashe ta dole ne a hukunta su. Taâaziyyata ga âyan uwa da abokan arziki.â
Bayan âyan saâoâi kadan Atiku ya goge sakon da ya wallafa a shafinsa na facebook inda ya bayyana dalilinsa na yin hakan.
A wani sako da ya aike a shafinsa na Hausa da aka tabbatar, tsohon mataimakin shugaban kasar ya nisanta kansa da sakon. Ya kuma bayyana cewa duk wani sako da ake yadawa a kafafen sada zumunta ba tare da baqaqen âA. A.” ba nasa ba ne.
âA yammacin yau na sami labarin cewa an yi wani rubutu wanda bai yarda da umarnina ba. Ina amfani da wannan don sanar da cewa duk wani post ba tare da A. A. ba daga gare ni bane. Allah ya kiyaye mu,â ya rubuta da harshen Hausa.
To sai dai kuma tsohon mataimakin shugaban kasar ya sha suka bayan matakin da ya dauka.