Za ku fahimci yadda APC ke da karfi a ranar zabe – Badaru

0
54

Gwamnan jihar Jigawa, Muhammad Badaru Abubakar ya ce jam’iyyun adawa za su fahimci banbancin jam’iyyar da jama’a suka zaba a2023.

Gwamnan ya bayyana hakan ne a ranar Juma’a yayin da yake jawabi ga dimbin jama’a a karamar hukumar Kaugama. Ya kuma mayar da martani ne kan lalata fastoci da allunan talla na jam’iyyar All Progressives Congress (APC) da ake zargin jam’iyyun adawa sun yi.

Ya ce jam’iyyar APC mai mulki a jihar ta samar da fili mai kyau ga daukacin jam’iyyun adawa na jihar.

A cewarsa: “Abin takaici ne matuka, a matsayinmu na jam’iyyar da ke mulki, ba mu ci zarafin kowa ba, ba mu lalata fosta da allunan wata jam’iyya ba, har yanzu wasu jam’iyyun adawa suna lalata namu.

“Jam’iyya mai karfi ba za ta shiga cikin wani fada ko lalata dukiyoyin ‘yan adawa ba amma kawai tana nuna bambance-bambance a ranar zabe.”

Badaru, ya kuma kara da cewa jam’iyyun adawa za su fahimci bambancin da ke tsakanin jam’iyyar da ta zabi jama’a da kuma wadanda aka raina.

Barnata allunan tallan na APC, ya bayyana cewa, ba zai shafi farin jinin jam’iyyar ba, illa kara yawan magoya bayanta

A cewarsa: “Abin takaici ne matuka, a matsayinmu na jam’iyyar da ke mulki, ba mu ci zarafin kowa ba, ba mu lalata fosta da allunan wata jam’iyya ba, har yanzu wasu jam’iyyun adawa suna lalata namu.

“Jam’iyya mai karfi ba za ta shiga cikin wani fada ko lalata dukiyoyin ‘yan adawa ba amma kawai tana nuna bambance-bambance a ranar zabe.