Zargin sace tiriliyan 89: Dan takara a Kano zai maka Buhari a kotu

0
59

Dan takarar da ke neman wakilcin al’ummar mazabar Kumbotso a majalisar dokokin tarayya a zaben 2023, Khalid Shettima Khalid ya bai wa shugaban kasa, Muhammad Buhari wa’adin sa’o’i 24 da ya dauki mataki a kan zargin da Honorabul Gudaji Kazaure ya yi kan zargin karkatar da Naira tiriliyan 89.

Khalid Shettima Khalid, ya bayyana haka ne a wata hira da manema labarai.

Khalid wanda ya tsaya takarar dan majalisar wakilai a karkashin jam’iyyar PRP.

Ya ce zargin da Honorabul Gudaji Kazaure ya yi yana da girma kuma binciken da shugaban kasa Muhammad Buhari ya yi shi ne ya zama wajibi a yi la’akari da halin kuncin da ‘yan Nijeriya ke ciki.

Ya ce badakalar da Honorabul Gudaji Kazaure ya bankado a babban bankin Nijeriya bai kamata a kunnen uwar shegu da ita ba.