2023: Manyan ‘yan takara na shafa wa juna kashin kaji

0
61

A daidai lokacin da ake ci gaba da gudanar da gangamin yakin neman zaben 2023, wanda aski ya zo gaban goshi, kowane dan takarar shugaban kasa ya kara matsa kaimi domin tallata manufofinsa ga ‘yan Nijeriya, inda a wannan makon abin ya kara zafi har ta kai ga manyan ‘yan takarar sun shafa wa junansu kashin kaji da nufin dusashe tauraron juna.

Dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar APC, Asiwaju Bola Ahmed Tinubu ya gargadi ‘yan Nijeriya a kan kar su sake su zabi PDP a zaben 2030, inda ya ce dan takararta na shugaban kasa, Atiku Abubakar dan rashawa ne da yake da kudirin sayar da Nijeriya idan har aka zabe shi a matsayin shugaban Nijeriya.

Tinubu ya bayyana haka ne a lolacin gangamin yakin neman zabensa a garin Ilorin da ke Jihar Kwara a tsakiyar makon nan.

Har ila yau, kwamitin yakin neman zaben APC ya bukaci a cafke tare da gurfanar da dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar PDP, Atiku Abubakar, wanda ya zarge shi lokacin da yake matsayin mataimakin shugaban kasa a tsakanin 1999 zuwa 2007, inda ya hada baki da mai gidansa a lokacin, Cif Olusegun Obasanjo, wajen sace dokiyar kasa ta amfani da sayen motoci na alfarma.

Kwamitin yakin neman zaben APC ya bukaci jami’an tsaro da su yi gaggawar damke Atiku tare da gurfanar da shi a gaban kuliya bisa kashe kudin kasa wanda ya yi amfani da sunayen kamfanoni masu rajista lokacin da yake matsayin mataimakin shugaban kasa.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here