‘Yan sanda sun ceto sarkin da aka yi garkuwa da shi a Filato

0
60

Rundunar ‘yansandan Jihar Filato, ta ce jami’anta sun cafke wadanda suka yi garkuwa da Sarkin kabilar Izere a karamar hukumar Jos ta Gabas, Dakta Azi Wakili.

A wata sanarwar da kakakin ‘yansandan jihar, DSP Alfred Alabo ya fitar, ya ce bayan samun kiran wayar gaggawa da suka yi daga caji ofis din Angware da ya bayyana cewa wasu ‘yan bindiga sun kutsa kai gidan Agwom Izere, Dakta Azi Wakili tare da yin garkuwa da shi.

Sanarwar ta ce, nan da nan rundunar ‘yansandan karkashin jagorancin DPO na Angware, SP Timothy Bebissa, suka isa wajen cikin gaggawa a yayin da jami’ansu guda ya gamu da rauni yayin da wani farar hula (Dan tsaron sa-kai) ya mutu sakamakon harbin da ‘yan bindigar suka masa.

Ya kara da cewa bisa kokarin ‘yansandan da hadin guiwar jami’an tsaro sa-kai na ‘yan banga sun ceto Sarkin daga hannun wadanda suka sace shi.

Ya kara da cewa wasu mutum biyu da ake zargi da hannu a lamarin sun shiga hannu.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here