HomeLabaraiYadda gobara ta kone gidan mai

Yadda gobara ta kone gidan mai

Date:

Related stories

INEC ta ce ba a kammala zabe a jihar Adamawa ba

Hukumar zaben Najeriya INEC, ta ayyana zaben gwamnan jihar...

An kashe ‘yan sanda 2, da dama sun raunata a wata arangama da sojoji a Taraba

A ranar Litin ne wasu sojoji suka kashe ‘yansanda...

Gwamna Zulum ya sake lashe zaben gwamna a jihar Borno

Sakamakon da hukumar zabe mai zaman kanta ta sanar...

Sojoji sun kashe hatsabinin dan ta’adda Umaru Nagona

Dakarun sojin Najeriya sun hallaka, Umaru Nagona, daya daga...

An kona gidan mawakin siyasa Rarara a Kano

Wasu da ake zargi ’yan daba ne sun banka...

Wani gidan mai ya kone bayan tashin gobara da ta kama injinan bayar da mai da wani gini da ke harabarsa a garin Akure, babban birnin Jihar Ondo.

Kakakin Hukumar a jihar, Ayodele Ajulo, ya ce wutar ta tashi ne sakamakon zafi da tankin ajiye mai a karkashin kasa ya dauka.

Ajulo wanda ya yi magana bayan kashe gobatar, ya ja hankalin masu gidajen mai da su rika yin hattara a duk lokacin da ake sauke mai zuwa tankunansu da ke karkashin kasa.

“Mun sha jan hankalin mutane musamman a wannan yanayi na zafi, saboda wuta ta kan tashi cikin sauki.

“Yana da matukar muhimmanci musamman ga masu gidajen mai da  su rika daukar dukkan matakan kariya don kauce wa asarar rayuka da dukiyoyi,” in ji shi.

Ya jinjina wa mazauna yankin da suka taimaka wajen ganin an kashe gobarar ba tare da an yi asarar rai ba.

Subscribe

- Never miss a story with notifications

- Gain full access to our premium content

- Browse free from up to 5 devices at once

Latest stories

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here