HomeLabaraiGwamnatin Kano ta ba wa ’yan magani mako 2 su bar kasuwar...

Gwamnatin Kano ta ba wa ’yan magani mako 2 su bar kasuwar sabon gari

Date:

Related stories

INEC ta ce ba a kammala zabe a jihar Adamawa ba

Hukumar zaben Najeriya INEC, ta ayyana zaben gwamnan jihar...

An kashe ‘yan sanda 2, da dama sun raunata a wata arangama da sojoji a Taraba

A ranar Litin ne wasu sojoji suka kashe ‘yansanda...

Gwamna Zulum ya sake lashe zaben gwamna a jihar Borno

Sakamakon da hukumar zabe mai zaman kanta ta sanar...

Sojoji sun kashe hatsabinin dan ta’adda Umaru Nagona

Dakarun sojin Najeriya sun hallaka, Umaru Nagona, daya daga...

An kona gidan mawakin siyasa Rarara a Kano

Wasu da ake zargi ’yan daba ne sun banka...

Gwamnan Jihar Kano Abdullahi Umar Ganduje, ya bai wa masu sayar da magani da ke kasuwar Sabon Gari da sauran wurare a birnin Kano, wa’adin mako biyu su koma sabuwar kasuwar magungunan da gwamnati ta gina.

Gwamnan ya bayyana hakan ne yayin bikin bude sabuwar kasuwar, in da ya ce ita ce kadai halastacciyar kasuwar magani da gwamnati ta amince da ita a yanzu a Jihar, don haka za ta rufe sauran.

wannan ce kadai halastacciya a yanzu, duk wanda muka samu ya saba umarnin, za mu dau mataki a kansa,” in ji Ganduje

Shi ma Shugaban Kungiyar Masu Harhada Magunguna ta Najeriya Ibrahim Babashehu Ahmad ya yi makamancin wancan gargadin, inda ya ce sashin tabbatar da doka na kungiyar zai tabbatar da rufe duk wani shago da ya yi taurin kan kin bin umarnin.

Shi ma dai Ministan Lafiya, Osagie Ehanire ya ce kasuwannin Sabon Gari da sauran manyan shagunan da ke sayar da magunguna a jihar, na taimakawa wajen karuwar magungunan jabu da miyagun kwayoyi, kuma zuwan kasuwar zai magance hakan.

Kasuwar dai ita ce irinta ta farko da aka kammala ginawa a Najeriya.

Subscribe

- Never miss a story with notifications

- Gain full access to our premium content

- Browse free from up to 5 devices at once

Latest stories

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here