An kwace na’urar BVAS guda 8 — INEC

0
66

Hukumar Zabe ta Kasa (INEC) ta ce ’yan daba sun tarwatsa wuraren zabe tare da da sace na’urar tantance masu zabe (BVAS) guda takwas a jihohin Delta da Katsina.

Shugaban INEC na kasa, Farfesa Mahmood Yakubu, ya bayyana cewa ’yan daba sun kwace na’urar BVAS guda shida a wani hari da suka kai rumfar zabe a Karamar Hukumar Safana a Jihar Katsina, inda suka yi.

An kai makamancin harin a Karamar Hukumar Oshimili a Jihar Delta, inda sauka yi awon gaba da na’urar BVAS guda biyu.

Ta sanar da haka ne a ranar Asabar yayin da yake jawabi game da zaben Shugaban Kasa da na ’yan Majalisar Tarayya da ke gudana.

Yakubu ya koka kan cewa, bayyane yake bata-garin sun maida hankalinsu ne kan na’urorin BVAS da ake amfani da su a wannan zabe.

Ya ce, ”Muna ba da tabbacin za mu ci gaba da yin abin da shi ne daidai, shi ya sa muka zabi yi wa ’yan kasa bayani a daidai wannan gabar, kuma za mu ci gaba da yin haka.

Ya ce hakki ne da ya rataya a wuyan INEC tabbatar da sahihin zabe a kasa.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here