Kotu na tuhumar wani mutum bisa laifin biyan karuwarsa da kudin bogi

0
88

Wata kotun majistare ta umurci a cigaba  da tsare wani da ake  zargi mai suna Oni Samuel a gidan gyaran hali da ke Akure babban birnin jihar Ondo bisa laifin damfarar wata karuwa mai suna Blessing Olaitan kudi Naira 120,000.

A ranar Alhamis, 9 ga Maris, 2023, wasu jami’an hukumar tsaro ta NSCDC, suka gurfanar da Samuel a gaban kuliya kan laifin da aka aikata a ranar 1 ga Maris, 2023, a layin Alagbaka na babban birnin Akure.

Olaitan wacce ta shaida wa kotun cewa ita kwararriyar karuwa ce, ta ce wadda ake zargin ya karbi kudin ne a wajenta na Naira 80,000 bayan ya yi lalata da ita a wani dare.

Ta kuma bayyana wa kotun cewa wanda ake kara ya yi alkawarin maida mata kudin tare da  N15,000 wanda shi ne “kudin kwanciyar da tai da shi.”

Ana zargin wadda ake kara ya yi amfani da wata hanyar damfara, wanda mai karar ta ce daga baya ta fahimta.

 

An gabatar da tuhume-tuhume biyu da suka shafi hada baki da sata a gaban kotu.

Takardar tuhumar ta zargi Oni Samuel da sauran jama’a da aikata laifin satar kudi N120,000 daga hannun Misis Blessing Olaitan, laifin da ya sabawa sashe na 516 na kundin laifuffuka na doka Cap 37, Vol. 1 Dokokin Jihar Ondo, 2006.

Wadanda ake tuhumar dai sun shigar da kara ne a kan zargin ba su da laifi, kamar yadda lauyan tsaro, Barista EO Nifemi, ya bukaci kotun da ta bayar da belinsa.

Mai gabatar da kara na hukumar NSCDC, Mista David Ebriku, ya ki amincewa da bukatar belin, ya kuma roki kotu da ta ci gaba da tsare wanda ake kara, yana mai jaddada cewa zai iya tsallake belin sannan kuma ya zama hadari ga al’umma.

A hukuncin da ya yanke, Alkalin Kotun Mai shari’a Tope Aladejana ya bayar da belin wanda ake kara a kan kudi Naira 200,000 tare da mutane biyu masu tsaya masa a kan kudi iri daya sannan ya dage sauraron karar zuwa ranar 17 ga Afrilu, 2023.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here