Na’ibin limamin masallacin Sultan Bello da ke Kaduna ya rasu

0
52

Allah Ya yi wa Na’ibin Limamin Babban Masallacin Sultan Bello da ke Kaduna, Malam Ibrahim Isah, rasuwa.

Alaramma Ibrahim Isa, wanda ya dade a matsayin Na’ibin Babban Limamin Masallacin Sultan Bello, ya rasu ne a safiyar ranar Laraba a Asibitin Garkuwa da ke Unguwar Sarki, Kaduna.

Kwamitin Gudanarwar na Masallacin Sultan Bello ya sanar da rasuwar tare da cewa, “Za a gudanar da Sallar Jana’izar Alaramma Ibrahim Isa bayan Sallar Azabar a harabar masallacin,” da ke Unguwar Sarkin Musulmi, Kaduna.

“Allah Ya jikan sa da rahama, ya kuma sanya shi a Aljanna Firdausi,” in ji sanarwar.

Marigayi Alaramma Ibrahim Isa ya shekara sama da 20 a matsayin Na’ibin Limamin Sultan Bello.

Yana daga cikin cikin masu jagorancin Sallar Juma’a da Sallar Tahajjud, kuma Allah Ya yi masa baiwar zakin murya wajen karatun Al-kur’ani.

Hakazalika, ya kasance yana jagorancin majalisin karatun Alkur’anin a masallacin bayan Sallar Asuba.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here