Tinubu ya yi haramar Umara, ya fara ziyarar kasashe uku gabanin rantsar da shi

0
50

Zababben shugaban kasa Asiwaju Bola Tinubu ya fara ziyarar kasashe uku gabanin rantsar da shi a ranar 29 ga watan Mayu.

Wata sanarwa da ta fito daga ofishin zababben shugaban kasa mai dauke da sa hannun Tunde Rahman ta nuna cewa yayin da Tinubu zai tafi, zai yi amfani da damar wajen tsara shirin mika mulki .

Tinubu, wanda zai yi amfani da damar ya huta a Paris da Landan, daga baya zai wuce Saudiyya don gudanar da aikin Hajji.

Sanarwar ta ci gaba da cewa: “Bayan yakin neman zabe da kakar zabe mai cike da gajiyawa, zababben shugaban kasa Asiwaju Bola Tinubu ya tafi kasar waje domin hutawa da kuma tsara shirin mika mulki gabanin rantsar da shi a ranar 29 ga watan Mayun 2023.

“Zababben shugaban kasar ya bar filin jirgin sama na Murtala Mohammed, Ikeja, zuwa Turai a daren Talata.

“Zababben shugaban kasar ya yanke shawarar ya huta ne bayan kammala yakin neman zabe da kuma lokacin zabe domin ya huta a Paris da Landan, yana shirye-shiryen zuwa Saudiyya don yin Umrah (karamin Hajji) da kuma azumin Ramadan da zai fara ranar Alhamis.

“Yayin da zai tafi, zababben shugaban kasar zai kuma yi amfani da damar wajen tsara shirin mika mulki. Ana sa ran zai dawo kasar nan ba da jimawa ba.”

“Muna umurtar kafafen yada labarai da su daina buga jita-jita da kuma da’awar da ba su da tabbas kuma a koyaushe su nemi karin haske daga ofishinmu,” in ji Rahman .

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here