Me ake ciki game da shirye-shiryen zaɓukan cike gurbi?

0
107

Hukumar zaɓe mai zaman kanta a Najeriya ta ce ta shirya tsaf domin kammala zaɓukan da suka rage, na gwamnoni da ‘yan majalisun tarayyar da kuma na jihohi.

Cikin wata tattaunawa da BBC, jami’ar INEC, Zainab Aminu Abubakar ta ce an kai mafi yawan kayan da ake buƙata zuwa ƙananan hukumomi a ranar Juma’a, kuma za a dangana da su gundumomin da za a yi zaɓen kafin wayewar garin Asabar.

“Muna son fara duk zaɓukan da ba a kai ga samun wanda ya yi nasara ba, da ƙarfe takwas na safe, ba ma son fara ko ɗaya a makare,” in ji Malama Zainab.

Cikin zaɓukan da za su ja hankali akwai na gwamna a jihar Adamawa, wanda za a fafata tsakanin gwamna mai ci Ahmadu Umaru Fintiri da Hajiya Aisha Dahiru Binani.

Haka nan kuma za a gudanar da zaɓen sanatoci a mazaɓu daban-daban a faɗin ƙasar, waɗanda suka haɗa da.

  • Mazaɓar Kebbi ta Arewa
  • Mazaɓar Sokoto ta Arewa
  • Mazaɓar Sokoto ta Kudu
  • Mazaɓar Sokoto ta Gabas
  • Mazaɓar Zamfara ta Tsakiya

A zaɓen da aka gudanar na ranar 25 Fabrairu, INEC ta tabbatar da zaɓukan da aka yi na mazaɓu 109.

Ya zuwa yanzu Jam’iyyar APC ce ta lashe mafi yawan kujeru da 55, sai PDP da take da kujeru 33, Jam’iyyar LP kuma ta samu kujeru 7, yayin da NNPP ke da 2.

Sauran jam’iyyun ƙasar kuma zuwa yanzu suna da kujera 4.

Shugaban INEC, Mahmood Yakubu a wani jawabi da ya yi, ya ce jam’iyyu takwas ne suka samar da sanatoci a zaɓen da ya gabata.

Jam’iyyun su ne APC, PDP, APGA, SDP, Labour, NNPP, ADC da YPP.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here