PSG ta dakatar da Messi saboda ya je Saudia Arabia ba tare da izini ba

0
99

Paris St Germain ta dakatar da Lionel Messi mako biyu, bayan da ya je Saudi Arabia ba tare da izinin ba.

Messi ba zai yi atisaye a PSG ba a tsawon hukuncin dakatarwar da aka yi masa.

An fahimci cewar kyaftin din Argentina, mai shekara 35, ya nemi izinin yin tafiyar domin kulla yarjejeniyar tallace-tallace ta kashin kansa, amma ba a amince ba.

Messi yana yi wa Saudi Arabia aikin jakadan hukumar yawon bude ido ta kasar.

Wanda ya lashe kofin duniya a Qatar a 2022, tsohon dan wasan Barcelona, kwantiraginsa zai kare a karshen kakar nan a PSG.

Mataimakin Barcelona, Rafael Yuste ya sanar a cikin watan Maris cewar sun tuntubi Messi kan batun ya koma Camp Nou da murza leda.

Messi ya ci kwallo 31 ya kuma bayar da 34 aka zura a raga a fafatawa 71 a dukkan karawar da ya yi wa PSG da lashe Ligue 1 a kakar da ta wuce.

Messi ba zaii buga karawa da Troyes da kuma Ajaccio ba, bayan da PSG ta bayar da tazarar maki biyar a teburi, saura wasa biyar a karkare gasar bana.

PSG na fatan lashe Ligue 1 na tara daga kaka 11 baya.

Lionel Messi ya dauki hukunci a hannunsa, wanda wasu ke ganin ya gama taka leda a PSG.

Dama kuma magoya bayan kungiyar ba sa kaunar Messi, kenan da kyar idan PSG za ta tsawaita yarjejeniyarsa.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here