Sujjadar Ronaldo bayan nasarar zura kwallo ta janyo cece-kuce

0
60

Salon murnar kwallon na Ronaldo dai ya kayatar da dimbin magoya bayansa musamman a cikin kasar ta Saudi  Arabia da ya koma takawa leda a farkon shekarar nan bayan rabuwa da Manchester United.

Yayin wasan na jiya dai, Ittihad ta fara zura kwallaye 2 a ragar Al Nassr gabanin kwallon Ghareeb da Ronaldo bayan dawowa daga hutun rabin lokaci ne kuma ana kuma gab da tashi daga wasa Ronaldon ya zura kwallon ta 3 wadda ke nuna tabbacin ci gaba da kasancewar Al Nassr a saman teburin gasar ta Saudi Lig da tazarar maki 3 dai dai lokacin da ya rage wasanni 2 a kammala kakar bana.

Wasu faifan bidiyo dai sun nuna yadda dan wasan mai shekaru 38 bayan zura kwallon kamar yadda ya saba ya yi fitaccen salón murnar da aka fi sanin shi da ita wato SIUU sannan ya kara da sujjada lamarin da ya sanya ilahirin filin wasan karadewa da sowa.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here