Ina maraba da zuwan Messi da Benzema Saudiyya – Ronaldo

0
89

A yayin da ake jita-jitar tafiyar wasu zaratan ’yan kwallon kafa na duniya zuwa Saudiyya, tauraron kungiyar Al-Nassr, Cristiano Ronaldo ya ce yana maraba da hakan.

Babbar gasar kwallon kafa ta kasar Saudiyya ka iya zama “daya daga cikin manyan gasa biyar a duniya” idan har aka dauko manyan ’yan wasa a duniya, in ji Cristiano Ronaldo.

A halin yanzu dai ana jijitar cewa Lionel Messi da Karim Benzema da Luka Modric za su koma murza leda a Saudiyya kuma Ronaldo ya ce yana “maraba” da zuwansu.

Gwarzon dan kwallon duniya har sau biyar ya koma Al-Nassr ne a watan Disamban bara, gabanin kammala wa’adin yarjejeniyarsa da United wadda za ta kare ne a shekara ta 2025.

A halin yanzu Paris St-Germain ta tabbatar da cewa Messi zai bar kungiyar a wannan bazarar, kuma dan kwallon na Argentina, mai shekaru 35 ya kasance jakadan yawon bude ido na kasar Saudiyya.

Ronaldo ya zura kwallo 14 a cikin wasa 16, inda ya taimaka wa kungiyarsa Al-Nassr ta kammala gasar a matsayi na biyu a kan tebur a yayin da Al Hilal ta lashe gasar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here