‘Yan sanda sun kama wanda ke safarar makamai da kayan abinci ga ‘yan bindiga a Abuja

0
108
CHICAGO, ILLINOIS - OCTOBER 19: Chicago police officers patrol downtown as the city celebrates the Chicago Sky's WNBA title on October 19, 2021 in Chicago, Illinois. The city has started to place police officers on unpaid leave for refusing to comply with the city's requirements that they report their COVID-19 vaccination status. Only about 65 percent of the city's police have complied with the order. (Photo by Scott Olson/Getty Images)

Jami’an rundunar ‘yan sanda sun kama wani da ake zargi kuma ake nema ruwa a jallo kan aikata miyagun laifuka da suka hada da safarar makamai da kayan abinci; kai rahoton sirri ga tawagar masu garkuwa da mutane da ke addabar babban birnin tarayya Abuja da kewaye.

Wanda ake zargin mai suna Mohammed Hamza (Auta) mai shekaru 25, rundunar da ke yaki da masu garkuwa da mutane ce ta kama shi a dajin Mongoro da ke kan iyaka da Jihar Neja.

Kakakin rundunar ‘yansandan babban birnin tarayya Abuja, SP Josephine Adeh, ta ce, wanda ake zargin ya dade da kasance cikin jerin sunayen wadanda rundunar ke nema ruwa a jallo, ana zarginshi ne da hannu wajen samar da bindigogi, alburusai da sauran makamai; kayan abinci da haramtattun kwayoyi ga ‘yan bindiga a maboyarsu daban-daban a cikin dazuzzuka ta hanyar amfani da babur.

Ta ce, rundunar ta kwato bindiga kirar AK47 guda daya, harsashan AK47, wayar hannu daya, kayan abinci da kuma babur wanda ba a yiwa rajista ba a hannun wanda ake zargin (Auta).

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here