Ba za mu biya ma’aikatan da Ganduje ya dauka aiki ba har sai mun tantance su – Gwamnatin Kano

0
109

Gwamnatin jihar Kano ta baiwa ma’aikatan jihar tabbacin fara biyan albashin watan Yuni a yau Litinin 26 ga watan Yuni, 2023.

Babban Akanta Janar na jihar, Alh. Abdulkadir Adussalam, ya bayyana haka a wata tattaunawa da manema labarai a Kano ranar Lahadi.

A cewarsa dukkan ma’aikatan gwamnati za su rika karbar albashin su ne a ranar 25 ga kowane wata kamar yadda gwamnan jihar, Abba Kabir Yusuf, ya umarta.

Abdulkadir ya ce sabbin ma’aikatan da aka dauka ba za su karbi albashin wannan wata ba saboda tantancewar da gwamnatin jihar za ta yi kan sahihancin tsarin daukar ma’aikata kafin su fara karbar albashi duk wata.

Akantan ya kuma bayar da tabbacin cewa duk wani kudi da ake cirewa ma’aikata a albashin su ba bisa ka’ida ba, gwamnati mai ci tana bayar da tabbacin kowa zai samu cikakken albashinsa har da ‘Yan fansho.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here