‘Yan sanda sun kama mutum 4 da ake zargi da safarar yara a Benue

0
55

Ƴan sanda a jihar Benue sun ce sun kama wasu mutum huɗu da ake zargi da safarar yara a Makurdi, babban birnin jihar. 

Mai magana da yawun ƴan sandan jihar, SP Catherine Anene, ta ce an samu nasarar kama mutanen ne bayan samun bayanai cewa suna safarar yara a wani sansanin ƴan gudun hijira a wasu sassa Makurdi. 

Jaridar Daily Trust ta ruwaito Anene na cewa sun kuma samu nasarar kama mutuanen huɗu bayan kai samame wuraren, sai dai jagoransu ya tsere. 

Ta ce waɗanda ake zargin sun bayyana cewa sun samar da wasu mata masu ciki, waɗanda idan suka haihu sai a karɓi jariran daga hannunsu, inda ake biyansu 150,000 kan kowane jariri. 

Ta kara da cewa sun samu nasarar gano wani yaro a gidan jagoran nasu wanda tun da farko iyayensa suka yi shigiyar cewa ya ɓata. 

Kakakin ƴan sandan ta shawarci iyaye cewa su sanya ido kan yaransu a kowane lokaci musamman ma yanzu da makarantu ke hutu.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here