Gwamnatin Tarayya ta tsawaita ranakun hutun Sallah

0
128
Tinubu
Tinubu

Gwamnatin Tarayya ta amince da sanya Alhamis, 11 ga watan Afrilun 2024 a cikin jerin kwanakin hutun karamar sallah da ta bayar.

Hakan dai na ƙunshe ne cikin wata sanarwa da Ministan Harkokin Cikin Gida, Dokta Olubunmi Tunji-Ojo ya fitar a safiyar wannan Talatar.

Wannan na zuwa ne sakamakon rashin ganin jinjirin watan Shawwal a jiya Litinin da zai kawo ƙarshen watan Ramadan.

Sanarwar mai ɗauke da sa hannun Babbar Sakatariya a Ma’ikatar Harkokin Cikin Gida, Dokta Aishetu Gogo Ndayako, tana kuma taya al’ummar Musulmi kammala Azumin watan Ramadana lafiya tare da fatan Allah Ya karɓi ibadu.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here