Majalisar dokoki ta gayyaci Dangote da BUA kan tsadar siminti

0
82

An bai wa Dangote da BUA da IBETO da sauran masu ruwa da tsaki wa’adin kwanaki 14 da su gurfana a gaban kwamitin hadin gwiwa na Majalisar dokoki kan tsadar farashin siminti a kasar.

Hakan ya biyo bayan gazawar da kamfanonin da wasu suka yi wajen gurfana wajen zaman binciken da aka yi ranar Talata.

An dai kafa kwamitin hadin gwiwar na majalisar dokokin wanda ya kunshi kwamitocin majalisar masu kula da ma’adanai da kasuwanci da masana’antu da kuma ayyuka na musamman domin ‘binciken ƙarin farashin siminti a Najeriya ba bisa ka’ida ba da kamfanonin yin simintin suka yi.

Majalisar ta kuma gayyaci ministan ma’adanai na kasa, Dele Alake, da ya gurfana gaban kwamitin bayan ya kasa bayyana a ranar Talata.

Majalisar ta kuma ba da umarnin cewa ministan ya bayyana ranar Talata, 21 ga Mayu yayin kuma da Dangote da BUA da IBETO da dai sauransu su kuma za su bayyana a ranar Litinin, 20 ga Mayu, 2024.

BBC

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here