Majalisar wakilai ta umarci CBN ya dakatar da harajin tsaron intanet

0
39

Mambobin majalisar wakilan Najeriya sun umarci babban bankin ƙasar, CBN ya janye aiwatar da harajin tsaro na intanet da zai cire kashi 0.5 cikin ɗari a duk lokacin da aka tura kuɗi ta asusun banki.

‘Yan majalisar sun bayyana matakin a matsayin abu mai sarƙaƙiya.

Wannan buƙatar dai na zuwa ne a matsayin martani ga wani kuduri kan bukatar gaggawa na dakatar da gyara aiwatar da harajin tsaron intanet, wanda Kingsley Chinda ya gabatar.

A cewar ƴan majalisar, CBN ya janye takardar aiwatar da tsarin da ya fitar , sannan kuma ya fayyace tsarin yadda ‘yan Najeriya za su fahimta.

Majalisar ta kuma nuna damuwa kan cewa za a aiwatar da dokar cikin kuskure idan ba a dauki matakin gaggawa ba, don magance matsalolin da ke tattare da fassarar umarnin na CBN da kuma dokar tsaro ta Intanet.

A ranar 6 ga watan Mayun shekarar 2024 ne babban bankin kasar CBN, ya fitar da wata sanarwa da ta umarci dukkan bankun da masu gudanar da hada-hadar kudi ta wayar salula su aiwatar da wani sabon harajin tsaro ta intanet saboda hana aikata laifuka ta intanet.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here