HomeLabaraiArtabun sojoji da Boko Haram ya sa an rufe hanyar Damboa

Artabun sojoji da Boko Haram ya sa an rufe hanyar Damboa

Date:

Related stories

INEC ta ayyana 29 ga Maris a matsayin ranar zaben cike gurbi a Adamawa

Hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC), ta...

IPOB ta umarci ‘yan kabilar Igbo da ke Legas su koma gida

Kungiyar masu rajin kafa ‘yantacciyar kasar Biafara ta IPOB,...

Sarkin Kano ya taya Abba Kabir murnar lashe zaben gwamnan Kano

Sarkin Kano Aminu Ado Bayero ya taya Abba Kabir...

Mata magoya bayan PDP na zanga-zangar kin amincewa da zabe a Kaduna

Wata tawagar mata sanye da bakaken kaya na jam’iyyar...

An rufe babbar hanyar Maiduguri zuwa Damboa bayan sojojin Rundunar Operation Hadin Kai sun yi artabu da mayakan Boko Haram.

Aminiya ta sami rahoto cewa ’yan ta’addan Boko Haram sun kai harin kwanton bauna ne a kan ayarin motocin fasinja da sojojin ke rakawa daga Maiduguri zuwa Damboa a daidai kauyen Falouja a Jihar Borno.

Wata majiyar tsaro ta ce ’yan ta’addar sun far wa sojojin da makamin roka, kafin su bi su da harbin bindiga.

Wata majiya a yankin da ta tsallake rijiya da baya, ta ce harin da ya haifar da musayar wuta tsakanin ’yan ta’addan da sojoji, ya tilasta wa fasinjojin da ke cikin ayarin motocin guje-guje domin tsira da rayukansu.

Majiyoyin sun ce soja daya ya mutu bayan da ya samu raunukan harbin bindiga, yayin da wasu uku da suka jikkata aka kai su Asibitin Damboa domin yi musu magani.

“Duk da harin da ’yan ta’addan suka kai, sojojin sun yi nasarar kare dukkan fasinjojin motocin,” in ji su.

Subscribe

- Never miss a story with notifications

- Gain full access to our premium content

- Browse free from up to 5 devices at once

Latest stories