HomeLabaraiBoko Haram ta kashe malaman makarantu dubu 2 da 295 daga 2009...

Boko Haram ta kashe malaman makarantu dubu 2 da 295 daga 2009 zuwa 2022

Date:

Related stories

Abba gida-gida ya lashe zaben gwamnan Kano

Hukumar Zabe ta Kasa, INEC ta sanar da cewa...

INEC na neman ta ce zaben gwamnan Kano ‘Inconclusive’ ne — Kwankwaso

Dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar NNPP, sanata Rabiu...

Zaben gwamnan Kano: Ratar kuri’ar da ke tsakanin NNPP da APC

Bayan bayyana sakamakon kananan hukumomi 44 na zaben gwamnan...

Jami’in tattara sakamakon zabe ya yanke jiki ya fadi a hedikwatar INEC a Kano

Jami’in tattara sakamakon zabe, Farfesa Muhammad Yushau na karamar...

Sakamakon zaben gwamnonin jihohin Najeriya

Wannan shafin zai rika kawo muku kammalallen sakamakon zaben...

Hukumar da ke kula da kwararrun malaman makarantu a Najeriya ta sanar da cewar hare haren ‘yan ta‘addan boko haram ya yi sanadiyyar mutuwar malaman makarantu dubu 2 da 295 tsakanin shekarar 2009 zuwa 2022.

Babban jami’in Hukumar Farfesa Josiah Olusegun Ajiboye ya gabatar da wadannan alkaluma masu tayar da hankali lokacin da ya ke jawabi wajen taron kungiyar malaman makarantu na kasa a Najeriyar.

Ajiboye ya ce ayyukan ta’addanci sun tilasta rufe makarantu sama da 1,500 abinda ya haramtawa dalibai sama da dubu 600 zuwa karatu domin samun ilimi.

Jami’in ya roki gwamnatin Najeriya da ta sake fasalin tsaron kasar domin samar da tsaron da ake bukata wajen kare malamai da dalibansu a sassan kasar da ake fama da tashe tashen hankula.

Ajiboye yace a matakin farko, ya dace gwamnatocin jihohi da kananan hukumomi da kuma tarayya da su gaggauta aiwattar da shirin kasa na samar da tsaro a makarantu ta hanyar ware wani kashe na kudin kasasfin su da zai kula da wannan bangare.

RFI

Subscribe

- Never miss a story with notifications

- Gain full access to our premium content

- Browse free from up to 5 devices at once

Latest stories