Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya jajantawa shugaba Yoon Suk-yeo, gwamnati da al’ummar Koriya ta Kudu bisa turmutsutsin da aka yi a ranar Asabar a gundumar Itaewon da ke birnin Seoul inda matasa da dama suka rasa rayukansu.
Akalla mutane 151 ne aka rahoto sun mutu, wasu 82 kuma suka samu raunuka yayin turmutsutsin da ya barke a gundumar yayin da suke bikin Halloween.
A sakon ta’aziyyarsa ga takwaransa na Koriya ta Kudu, Buhari ya aika da addu’o’in fatan samun sauki ga wadanda suka jikkata.