Sojojin Najeriya sun kama kwamandan ISWAP a Neja

0
66

Rundunar sojin Najeriya ta tabbatar da kashe ƴan bindiga bakwai a Jihar Kaduna tare da ƙwato makamai.

Haka kuma wasu rahotannin na cewa sojojin sun daƙile wani hari da aka kai musu a wani sansanin su da ke Ƙaramar Hukumar Borgu ta Jihar Neja har sun kama kwamandan ƙungiyar ISWAP.

A wani saƙo da rundunar sojin Najeriya ta wallafa a shafinta na Facebbok, ta bayyana cewa tun da farko dakarun Operation Safe Forest Sanity ne suka ƙaddamar da wani samame a Maidaro da Tudun Kagi da Kusharki da kuma Anguwan Madaki duka da ke Ƙaramar Hukumar Birnin Gwari.

A yayin samamen, sojojin sun yi musayar wuta da ƴan bindigar inda suka kashe ƴan bindigar huɗu tare da ƙwato bindigogi ƙirar AK-47 guda biyu da lodi biyu na harsasai samfarin 7.62mm da kuma bindiga ƙirar Pump Action ɗaya da harsasai uku da ƙananan bindigogi na gargajiya uku da babura huɗu.