HomeLabarai‘Yan bindiga sun yi garkuwa da matar kwamandan NSCDC a jihar Nasarawa

‘Yan bindiga sun yi garkuwa da matar kwamandan NSCDC a jihar Nasarawa

Date:

Related stories

Abba gida-gida ya lashe zaben gwamnan Kano

Hukumar Zabe ta Kasa, INEC ta sanar da cewa...

INEC na neman ta ce zaben gwamnan Kano ‘Inconclusive’ ne — Kwankwaso

Dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar NNPP, sanata Rabiu...

Zaben gwamnan Kano: Ratar kuri’ar da ke tsakanin NNPP da APC

Bayan bayyana sakamakon kananan hukumomi 44 na zaben gwamnan...

Jami’in tattara sakamakon zabe ya yanke jiki ya fadi a hedikwatar INEC a Kano

Jami’in tattara sakamakon zabe, Farfesa Muhammad Yushau na karamar...

Sakamakon zaben gwamnonin jihohin Najeriya

Wannan shafin zai rika kawo muku kammalallen sakamakon zaben...

Wasu ‘yan bindiga sun sace matar babban kwamandan rundunar tattara bayanan sirri ta rundunar tsaro da bayar da agaji ta Nijeriya da aka fi sani da Civil Defence, (NSCDC) a Jihar Nasarawa.

Wakilin jaridar Daily trust ya bayyana cewa masu garkuwa da mutane dauke da bindigogi kirar AK-47, sun kutsa cikin gidan kwamandan inda suka fara harbe-harbe don tsorata jama’a kafin su tafi da uwargidan ta sa.

An samu labarin harbin kanin Kwamandan wanda kuma ma’aikacin NSCDC ne a lokacin da lamarin ya faru a garin Lafia babban birnin jihar Nasarawa.

Yanzu haka ana jinyarsa a wani asibiti da ba a bayyana sunansa ba da ke garin Lafia, babban birnin jihar Nasarawa.

Lamarin dai kamar yadda aka rawaito, ya faru ne a ranar Laraba da misalin karfe 8:30 na dare da yake tabbatar da faruwar lamarin ga manema labarai a ranar Alhamis, jami’in hulda da jama’a na hukumar NSCDC reshen jihar Nasarawa, Mista Jerry Victor, ya bayyana cewa har yanzu ba a san inda ‘yan bindigar suke ba, kuma basu tuntubi kowa ba.

Subscribe

- Never miss a story with notifications

- Gain full access to our premium content

- Browse free from up to 5 devices at once

Latest stories