HomeLabaraiINEC ta samar da tsarin yadda ‘yan gudun hijira za su yi...

INEC ta samar da tsarin yadda ‘yan gudun hijira za su yi zabe a Zamfara

Date:

Related stories

Abba gida-gida ya lashe zaben gwamnan Kano

Hukumar Zabe ta Kasa, INEC ta sanar da cewa...

INEC na neman ta ce zaben gwamnan Kano ‘Inconclusive’ ne — Kwankwaso

Dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar NNPP, sanata Rabiu...

Zaben gwamnan Kano: Ratar kuri’ar da ke tsakanin NNPP da APC

Bayan bayyana sakamakon kananan hukumomi 44 na zaben gwamnan...

Jami’in tattara sakamakon zabe ya yanke jiki ya fadi a hedikwatar INEC a Kano

Jami’in tattara sakamakon zabe, Farfesa Muhammad Yushau na karamar...

Sakamakon zaben gwamnonin jihohin Najeriya

Wannan shafin zai rika kawo muku kammalallen sakamakon zaben...

Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta (INEC) a Jihar Zamafara ta sanar da cewar ta samar da tsarin yadda ‘yan gudun hijira da kuma al’ummar da hare-haren ‘yan bindiga ya kore su, za su kada kuri’unsu a zaben 2023.

Kwamishinan hukumar a jihar, Farfesa Sa’idu Ahmad ya sanar da hakan a hirarsa da manema labarai a jihar a kan shirye-shiyen da hukumar ke yi na fara lika sunayen masu jefa kuri’a a jihar.

A cewar Farfesa Ahmad, rashin tsaro ya janyo wa hukumar rashin fara gudanar da ayykanta na shirye-shiyen zaben a kan lokacin da ya dace kafin zuwan zaben na 2023, inda ya ce hakan ya zamowa hukumar babban kalubale wajen shiga lungu da sako na jihar don yin rijistar masu karbar katin zabe, musamman saboda kalubalen rashin tsaro.

kwamishinan ya ce duk da wannan kalubalen na rashin tsaron, hukumar ta samu nasarar yi wa adadin wadanda suka kai munzalin jefa kuri’a guda 211,970 a jihar.

Ya kara da cewa “Muna da kididdigar, musamman a kananan hukumomin 13 zuwa 14, akwai mutanen da dama da hare-haren na ‘yan bindiga ya tilasta su tashi daga yankunansu.

 Farfesa Sa’idu ya kuma bayyana cewa, hukumar ta fara karbar kayan gudanar da zaben masu muhimma ci domin gudanar da zabukan 2023.

Ya sanar da cewa, hukumar ta kuma magance yin rijistar katin zabe fiye da daya, inda ya ce, hukumar za ta kuma kafe sunayen masu jefa kuri’a daga ranar 12 ga watan Nuwamba 2022 zuwa ranar 19 ga watan Nuwamba, 2022.

Subscribe

- Never miss a story with notifications

- Gain full access to our premium content

- Browse free from up to 5 devices at once

Latest stories