HomeLabaraiHarbin ma'aikaciyar jinkai: Zulum ya jajanta wa majalisar dinkin Duniya

Harbin ma’aikaciyar jinkai: Zulum ya jajanta wa majalisar dinkin Duniya

Date:

Related stories

INEC ta ce ba a kammala zabe a jihar Adamawa ba

Hukumar zaben Najeriya INEC, ta ayyana zaben gwamnan jihar...

An kashe ‘yan sanda 2, da dama sun raunata a wata arangama da sojoji a Taraba

A ranar Litin ne wasu sojoji suka kashe ‘yansanda...

Gwamna Zulum ya sake lashe zaben gwamna a jihar Borno

Sakamakon da hukumar zabe mai zaman kanta ta sanar...

Sojoji sun kashe hatsabinin dan ta’adda Umaru Nagona

Dakarun sojin Najeriya sun hallaka, Umaru Nagona, daya daga...

An kona gidan mawakin siyasa Rarara a Kano

Wasu da ake zargi ’yan daba ne sun banka...

Gwamnan jihar Borno, Babagana Umara Zulum ya aika wa Majalisar Dikin Duniya sakon jaje bisa kisan wata ma’aikaciyar jinkai ’yar kasar Habasha, Alem da wani soja ya yi.

Gwamnan ya aika da sakon ta’azziyar ne ta wata wasika da ya aikewa Mista Matthias Schmale, Wakilin Majalisar a Najeriya.

Zulum ya bayyana matukar bakin ciki da alhinin abin da ya faru na harbin da sojan ya yi a garin Dambowa a ranar Alhamis.

Harbin dai ya halaka Misis Alem Museta da kuma abokan aikinta na kungiyar agaji ta Likitoci mai suna ‘Medicine de Monde’.

“Ina mika ta’aziyyata ga iyalan wannan mata da ta rasu, da kuma sauran iyalan sojojin da suka mutu yayin da suke kokarin rike wannan soja daga aikata wannan danyen aiki”. In ji gwamna Zulum.

Gwamnan ya kuma ce, an garzaya da matukin jirgin da shi ma harbin ya rutsa da shi asibiti, yana kuma samun kulawa, kuma gwamnati za ta ci gaba kulawa da shi har sai ya samu lafiya.

Sannan gwamnan ya ce, su na nan, su na binciken lamarin, ya kuma tabbar da cewa za su dauki matakin kula da lafiyar kwakwalwar sojojin da ke bakin daga.

Ana zargin sojan ya yi harbin ya larurar tabin hankali.

Subscribe

- Never miss a story with notifications

- Gain full access to our premium content

- Browse free from up to 5 devices at once

Latest stories