HomeLabaraiHako mai a Kolmani: Gwamnonin Bauchi da Gombe sun amince su yi...

Hako mai a Kolmani: Gwamnonin Bauchi da Gombe sun amince su yi aiki tare

Date:

Related stories

INEC ta ayyana 29 ga Maris a matsayin ranar zaben cike gurbi a Adamawa

Hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC), ta...

IPOB ta umarci ‘yan kabilar Igbo da ke Legas su koma gida

Kungiyar masu rajin kafa ‘yantacciyar kasar Biafara ta IPOB,...

Sarkin Kano ya taya Abba Kabir murnar lashe zaben gwamnan Kano

Sarkin Kano Aminu Ado Bayero ya taya Abba Kabir...

Mata magoya bayan PDP na zanga-zangar kin amincewa da zabe a Kaduna

Wata tawagar mata sanye da bakaken kaya na jam’iyyar...

Gwamnonin jihohin Bauchi da Gombe sun amince za su yi aiki tare domin tabbatar da nasarar aikin hako danyen mai a yankin Kolmani.

Da yake jawabi a wajen bikin kaddamar da aikin, Gwamnan Bauchi Bala Mohammed, ya ce, duk da dai Rafin Kolmani na kan iyaka ne tsakanin Karamar Hukumar Alkaleri a Bauchi da Karamar Hukumar Akko a Gombe, akwai fahimtar juna a tsakaninsu.

Ya ce, “Za mu ci gaba da mara wa kokarin Gwamnatin Tarayya baya da martaba tsare-tsarenta na kiyaye rayuka da dukiyoyin jama’a da kuma ci gaban tattalin arziki.”

Shi ma Gwamnan Gombe, Inuwa Yahaya, ya ba da tabbacin jiharsa za ta ba da hadin kan da ya dace a matakai daban-daban domin cim ma nasarar wannan aiki.

Kolmani yankin ne da ke tsakanin Jihar Bauchi da Gombe, inda a nan Shugaba Muhammadu Buhari ya kaddamar da aikin hako mai a ranar Laraba.

A watan Oktoban 2019, Kamfanin NNPC ya ba da sanarwar gano danyen mai da gas Rafin Kolmani.

Wannan shi ne karon farko da aikin hako mai zai gudana a yankin da ma Arewa maso Gabashin Najeriya.

Subscribe

- Never miss a story with notifications

- Gain full access to our premium content

- Browse free from up to 5 devices at once

Latest stories