HomeLabaraiLabaran DuniyaHarin Masallaci: Dan sanda ne ya kashe mutum 101 da bom a...

Harin Masallaci: Dan sanda ne ya kashe mutum 101 da bom a Pakistan

Date:

Related stories

INEC ta ayyana 29 ga Maris a matsayin ranar zaben cike gurbi a Adamawa

Hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC), ta...

IPOB ta umarci ‘yan kabilar Igbo da ke Legas su koma gida

Kungiyar masu rajin kafa ‘yantacciyar kasar Biafara ta IPOB,...

Sarkin Kano ya taya Abba Kabir murnar lashe zaben gwamnan Kano

Sarkin Kano Aminu Ado Bayero ya taya Abba Kabir...

Mata magoya bayan PDP na zanga-zangar kin amincewa da zabe a Kaduna

Wata tawagar mata sanye da bakaken kaya na jam’iyyar...

An gano cewa dan kunar bakin waken da ya kashe mutum 101 a harin bom a masallacin hedikwatar ’yan sanda a kasar Pakistan yana sanye ne da kayan ’yan sanda.

Hukumar ’yan sandan Pakistan ta sanar a ranar Alhamis cewa, “Wadanda ke gadi ba su bincike shi ba saboda yana sanye da kakin ’yan sanda… Wannan ce matsalar,” in ji Moazzam Jah Ansari, Shugaba Rundunar ’Yan Sandan Lardin Khyber Pakhtunkhwa.

Ya shaida wa manema labarai cewa ‘yan sanda sun fara gano bayanan nan kunar bakin waken ne bayan tsuntsaye jikin kansa da kuma kamanta shi da hotunan harin da aka dauka ta CCTV.

Ya yi zargin, “Akwai hadin baki,” yana mai bayyana cewa harin na ranar Litinin ba dan kunar bakin waken kadai ne ya shirya shi ba.

Daruruwan ’yan sanda ne ke Sallah a hedikwatar rundunar da ke yankin yankin Peshawar, lokacin da dan kunar bakin waken ya tayar da bom din, wanda ya da ginin ya fadi a kansu ya kashe su.

A halin yanzu dai hukumomin kasar na gudanar da bincike kan musabbabin harin a wurin da ke da tsaurara matakan tsaro a birnin da ke mazaunin hukumomin yaki da ta’addanci da na binciken kwakwaf.

Harin dai shi ne mafi muni a cikin shekaru a Pakistan.

Subscribe

- Never miss a story with notifications

- Gain full access to our premium content

- Browse free from up to 5 devices at once

Latest stories

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here