Gawuna ya taya shugaban Najeriya mai jiran gado, Bola Tunibu, murnar lashe zabe

0
52

Alhaji Nasiru Gawuna, mataimakin gwamnan jihar Kano kuma dan takarar gwamna na jam’iyyar APC, ya taya zababben shugaban kasa, Sanata Bola Tinubu, da mataimakinsa, Sanata Kashim Shettima, murnar nasarar da suka samu a zaben ranar Asabar.

Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da babban sakataren yada labarai na mataimakin gwamnan, Malam Hassan Musa-Fagge ya fitar a ranar Laraba a Kano.

 

Gawuna ya kuma yabawa magoya bayan jam’iyyar da suka bayar da ruwan kuri’unsu ga ‘yan takarar jam’iyyar, ya sake yin kira gare su da su sake fitowa su kada kuri’unsu a zaben gwamnoni da na ‘yan majalisar jiha da za a yi a ranar 11 ga watan Maris.

“Kun fito a baya kuma mun yi imanin za ku sake yin hakan a cikin tsarin siyasa na zaman lafiya don tabbatar da nasarar ‘yan takararmu masu neman mukamai daban-daban a jihar” in ji shi.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here