Ma’aikatan sufurin jiragen sama sun fara yajin aikin gargadi a Najeriya

0
74

Yau Litinin ma’aikatan fannin sufurin jiragen sama a Najeriya za su fara yajin aikin kwanaki biyu, domin neman a kyautata musu yanayin aiki da kuma wasu kudade da suke bin gwamnati.

Tun a ranar Juma’ar da ta gabata, ma’aikatan sufurin saman suka sha alwashin tsunduma yajin aikin, wanda karo nan a biyu kenan da suke daukar irin matakin a shekarar bana.

Ma’aikatan da suka hada da matuka jirgin sama, da injiniyoyi da masu kula da zirga-zirgar jiragen saman a sararin samaniya, da dai sauran ma’aikatan filin jiragen, sun ce za su  kaurace wa aiki ne a ranakun yau Litinin da gobe Talata bisa la’akari da basukan da suke bi, da kuma matakin gwamnati na rusa ofisoshin wasu hukumomin sufurin jiragen sama a  Legas domin fadada filin jirgin saman birnin.

Fannin sufurin jiragen sama a Najeriya na fuskantar matsaloli da suka hada da rashin ingancin kayayyakin aiki a wasu filayen jiragen, da karancin mai da ke takaita  zirga-zirgarsu a cikin gida, da kuma rashin isassun kudaden kasashen waje wanda ya sa kamfanonin jirage na kasa na kasa biyan wani kaso na kudaden da suka samu daga sayar da tikitinsu.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here