Dalibin islamiyya ya gina gadar Naira miliyan 12.8 a Ogun

0
60

Dosumu Kazeem, dalibin makarantar Madrasatul Da’Watul Haqq, Leme, Abeokuta, ya bayar da gudummawar gina gadar da kudinta ya kai miliyan 12.8 ga al’ummar Itesiwaju da ke Idi-Aba, Oke-Odo, yankin Olokuta a Abeokuta, Jihar Ogun.

Gadar dai ta hada al’umma zuwa karshen Olokuta na Idi-Aba, a karamar hukumar Abeokuta ta Kudu.

An tattaro cewa gadar ita ce hanya daya tilo ga daliban makarantar Baptist Girls College, Abeokuta Grammar School da sauransu.

Mai bayar da tallafin mai shekaru 40, wanda kuma manomi ne, ya ce ya gudanar da aikin ne tallafin daga iyayensa domin rage radadin da yaran makaranta da sauran al’umma ke ciki.

Wannan aiki, kamar yadda ya bayyana, an ba shi fifiko ne a cikin kudin aikin gidansa na kashin kansa, kamar yadda ya fasa yin aikin Umrah zuwa Saudiyya don ba shi damar kammala gadar.

Kazeem ya bayyana haka ne a lokacin da yake zantawa da manema labarai bayan kammala aikin, inda ya ce ya kwashe shekaru uku ana gudanar da aikin, inda ya ce ya aro kudi daga iyayensa kafin ya kai ga kammmala  yin aikin.

“Game da shi kuma na yanke shawarar cewa zan iya yin hakan kuma ba zan jira ba har sai an samu matsala ba. Ba ni da mota tawa ko babur. Miliyan 12.8 na iya yi min abubuwa da dama da suka hada da motar da ta dace, amma ina son mutane su amfana da ni ta hanyar aikin.

“Ban kammala gidana a unguwar da na fara ba a shekarar 2017.”

Da yake jawabi yayin ziyarar aikin, malaminsa na ilimin Larabci da Ilimin Addinin Musulunci kuma babban limamin Masallacin Da’Watul Haqq, Leme, Imam Ishaq Muhammadu Awwal, ya ce wannan karamcin da manomin ya yi shi ke nuni da karantarwar Musulunci.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here