Ana fargabar dalibai 2 sun mutu a kifewar kwale-kwale a Kano

0
95

Ana can ana ci gaba da zaman alhini a Kano, bayan da kifewar wani kwale-kwale dauke da wasu ɗalibai a madatsar ruwan karamar hukumar Dambatta. 

Ana fargabar cewa mutum biyu sun rasa rayukansu a hatsarin. 

Lamarin ya ritsa da su ne bayan da suka shiga kwale-kwalen don yin shawagi a cikin ruwan da ke kusa da makarantar. 

Ɗalibai uku ne a cikin jirgin ruwan sai kuma direba, amma dalibi daya ya kubuta tare da direban, yayin da biyu kuma suka bata.

Masu aikin ceto mutum biyun da suka bata, sun fito da gawar mutum guda.

Sai dai har yanzu ba a kai ga gano gawar mutum dayan ba.

Madatsar ruwan da lamarin ya auku da ake kira Thomas Dam, na da tazarar kilomita biyar da kwalejin.

Ana yawan samun haɗarin jiragen ruwa a Najeriya, al’amarin da ake alakantawa da yawan amfani da matattun jirage da kuma rashin bin tsari wajen amfani da jiragen ruwan.

BBC

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here