Ina cike da mamakin yadda Haaland yake nuna bajintar sa – Gardiola

0
76

Kawo yanzu a wannan kakar dai, Haaland ya zura kwallon sa ta 50 a City a karawar da suka yi da Fulham. 

Dan wasan na Norway a yanzu na kokarin kafa tarihin yawan zura kwallo a gasar Firimiyar Ingila a kaka guda, ganin yadda ya taddo yawan kwallaye 34 da ‘yan wasa Alan Shearer da kuma Andrew Cole suka ci a gasar.

A zantawar da Guardiola ya yi da manema labarai gabanin wasan su da West Ham United a Laraban nan, ya ce abinda Haaland ya yi ya basu mamaki amma kuma kila shi baiji mamakin abinda ya yi ba ganin ya taba yin hakan a wasu gasanni da ya fafata.

Ya ce suna fatan dan wasan zai ci gaba da nuna bajinta wajen zura kwallo daga yanzu har zuwa karshen kakar wasan bana. 

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here