Tinubu ya rushe dukkan hukumomin gudanarwar ma’aikatu da hukumomin gwamnati

0
87

Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu ya amince da rushe dukkan hukumomin gudanarwa na ma’aikatu da kamfanonin Gwamnatin Tarayya ba tare da bata lokaci ba.

Hakan dai na kunshe ne a cikin wata sanarwa da Daraktan Yada Labarai a Ofishin Sakataren Gwamnatin Tarayya, Willie Bassey ya fitar da maraicen Litinin.

Matakin kuma na zuwa ne jim kadan bayan Shugaban ya sauke dukkan manyan Hafsoshin Tsaro na Kasa.

Muna tafe da karin bayani…

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here