Erdogan ya yi kira ga Musulmai su hada kai don yakar makiya Musulunci

0
93
Erdogan
Erdogan

Shugaban Turkiyya Recep Tayyip Erdogan ya jaddada bukatar hada kai domin daukar mataki kan kin jinin addinin Musulunci da kyamar baki a kasashen Yamma.

“Mummunan hari kan littafinmu mai tsarki, Alkur’ani a Sweden a ranar Idin Babbar Sallah na nuna wani nau’i kin jinin Musulunci mai ban tsaro,” kamar yadda ya bayyana a wani bidiyo wanda aka tura wa wani taro karo na 46 na shekara-shekara na Kungiyar Masana Falsafa ‘yan asalin Pakistan da ke a Arewacin Amurka a ranar Asabar.

Erdogan ya jaddada cewa hakkin duka Musulmi ne kiyaye afkuwar irin wannan rashin hankali a nan gaba.

“Dukanmu Musulmai na da babbar rawar da za mu taka domin tabbatar da cewa irin wannan lamari, wanda a Turkiyya muka mayar da kakkausan martani a kansa, bai sake faruwa ba. Idan muka hada kai don daukar mataki da zuciya daya da hannu daya, babu wani a duniya da ya isa ya ci mutuncin Musulmi,” in ji shi.

Erdogan ya kuma kara tunatar da dangantaka mai karfi da ke tsakanin Turkiyya da Pakistan wadanda ya kira ‘yan uwan juna.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here