Najeriya na bin Nijar bashin sama da naira biliyan 4 na wutar lantarki

0
164
wutar lantarki

Wani rahoton da hukumar kula da wutar lantarki ta Najeriya ta fitar ya ce yanzu haka ƙasar tana bin jamhuriyar Nijar kuɗin lantarki har naira biliyan 4.22. 

Madatsar ruwa ta Kainji da ke jihar Neja ce take samar wa jamhuriyar Nijar lantarkin.

Nijar tana ƙoƙarin kammala madatsar ruwanta kafin ƙarshen 2025 don magance dogaro kan Najeriya wajen samun lantarki. 

Rahoton ya ce Nijar tana daga cikin abokan cinikin lantarki na Najeriya da ba su biya maƙudan kuɗin wutar da suka sha ba.

Hukumar kula da lantarkin ta Najeriya dai ta nemi a ɗauki matakin ganin waɗanda lamarin ya shafa sun biya kuɗaɗen lantarkin da suka sha.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here