Babu wani shiri na sake dawo da tallafin mai – Gwamnatin tarayya

0
129
man fetur
man fetur

Gwamnatin tarayya ta ce babu wani shirin sake maido da tallafin man da ta cire jim kadan bayan karbar ragamar mulki, duk kuwa da yadda al’ummar kasar ke korafe korafe a game da irin halin kuncin da matakin ya jefa su.


Babban mai taimaka wa shugaba Bola Tinubu a fannin yada labarai, Tope Ajayi ne ya bayyana haka, a lokacin da yake mayar da martani ga rade-radin da ake yi cewa gwamnatin kasar za ta lashe aman da ta yi a game da wannan mataki nata.

Tun da farko sai da shugaba Tinubu, ta bakin kakakinsa, Ajuri Ngalale ya tabbatar wa da ‘yan Najeriya cewa ba za a kara farashin man fetur ba.

“Shugaba Tinubu ya gamsu bisa ga bayanin da ke gabansa cewa za mu iya kula da farashin a yanzu ba tare da musanya tsarin da aka bullo da shi na yanzu ba ta hanyar hanzarta tsaftace rashin aiki bangaren man fetur,” in ji Ajayi.

Tun a ranar 29 ga watan Mayu da aka rantsar da Tinubu a matsayin shugaban kasa a lokacin ya bayyana cire tallafin man fetur, farashin da ya ninka sau uku: daga kimanin N200 zuwa kusan N600.

Hakan ya haifar da hauhawar farashin kayayyaki da kuma tabarbarewar tattalin arzikin miliyoyin ‘yan Najeriya.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here