Shettima zai wakilci Tinubu a taron kasashen BRICS a kasar Afrika ta Kudu

0
103
Kashim Shettima
Kashim Shettima

Mataimakin shugaban ƙasa, Sanata Kashim Shettima ya bar Abuja zuwa Afrika ta Kudu domin wakiltan shugaba Bola Tinubu a taron shugabannin ƙasashen BRICS karo na 15 da za a yi.

Shettima zai bi sahun sauran shugabannin siyasa da ƴan kasuwa a faɗin duniya domin halartar taron a Afrika ta Kudu wanda zai gudana daga 22 ga watan Agusta zuwa 24.

Taron zai tattauna ne kan batutuwan da suka shafi kasuwanci, saukaka zuba jari, samun ci gaba, kirkire-kirkire da kuma garanbawul na yadda ake shugabanci a faɗin duniya.

Har ila yau, taron zai duba batun ci gaba da tallafawa ƙasashen Afrika da kuma kudancin duniya.

Manyan shugabanni da za su halarci taron sun haɗa da Shugaban Afrika ta Kudu, Cyril Ramaphosa, Shugaba Xi Jinping na China, Shugaban Brazil, Luiz da Silva da kuma Firaministan Indiya Narendra Modi.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here