CBN za ta yiwa daraktoci 8 ritaya, ma’aikata da dama za su koma Legas

0
124

Za a sallami akalla daraktoci takwas da ke aiki a Babban Bankin Najeriya CBN bisa wani dalili da har yanzu ba a gama fayyacewa ba.

Majiyarmu a bankin ta tabbatar mana da cewa wasu daga cikin wadanda za a sallamar har an miƙa musu takarda tun ranar Juma’a 15 ga Maris, 2024.

“Abin da na sani dai shi ne tabbas, wasu tun ranar Juma’a aka aika musu wasikun ritaya daga aiki.

“Sai dai abin da har yanzu ba mu tantance ba shi ne, shin ritayar ta gaggawace, ko kuma ta kawo ƙarshen yarjejeniyar aiki ce da aka kulla da su,” in ji majiyar.

Sai dai abin da majiyar ba ta fayyace ba shi ne dalilin sallamar waɗannan manyan ma’aikata daga aiki.

Kazalika, ba ta tabbatar da cewa laifi suka yi aka dakatar da su ko kuma an same su da hannu wurin aikata ba daidai ba.

Wata majiyar kuma ta ce “ina ganin babban dalilin sallamar waɗannan daraktoci shi ne, sun yi aiki tare da tsohon gwamnan da aka tsige watannin baya, wato ana ganin kamar na hannun daman zamanin Godwin Emefiele ne.”

Tun Yammacin ranar Alhamis dai ake ta gunagunin sallamar manyan daraktocin a tsakanin ma’aikatan babban bankin.

Rashin sanar da ‘yan jarida gaskiyar abin da ke faruwa kan dalilan wannan taƙaddama na ci gaba da zama barazana ga sauran ma’aikatan bankin, domin kuwa suna ganin kamar wannan wata gobara ce da ta taso daga kogi, kuma ƙila ta shafi da yawa daga cikinsu.

Binciken Aminiya ya bankaɗo cewa wasu daga cikin daraktocin sun lashi takobin kalubalantar hukumar bankin kan sallamarsu, yayin da wasu suka ce za su fawwala wa Allah, su yi tafiyarsu domin aiki a CBN yanzu ya zama kamar aiki a kan ƙaya.

Wani da bai so mu ambaci sunansa ba ya bayyana mana cewa “ Idan har aka ba ni takardar sallama, zan karba in yi wa Allah godiya bisa damar da Ya ba ni na yin aiki a wurin, da kuma irin gudunmawar da na bayar a wurin kawai in sa takalmi na in yi gaba, in ci gaba da rayuwata.”

Ana ganin cewa bankin na shirin ɗauko waɗansu da suka yi aiki suka yi ritaya a wasu wuraren domin maye gurbin wadanda aka sallama.

Akwai rade-radin cewa za a ɗauko Mataimakin Shugaban Rundunar ‘Yan Sandan Najeriya, Hakeem Odumosu mai ritaya wanda ya riƙe matsayin Kwamishinan ‘Yan Sanda a Jihar Legas domin riƙe ɓangaren tsaro na CBN.

AMINIYA

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here