Tinubu ya kaddamar da tsarin karbar kaya bashi ga yan Najeriya

0
182
Tinubu
Tinubu

Shugaban Najeriya, Bola Tinubu ya ƙaddamar da kashin farko na tsarin karɓar bashin kaya ga ƴan ƙasar.

Bayanin hakan na ƙunshe cikin sanarwar da mai bai wa shugaban shawara kan yaɗa labarai, Ajuri Ngelale ya fitar.

Tsarin zai bai wa al’umma damar inganta rayuwarsu ta hanyar samun bashin kayyaki inda za su riƙa biya sannu a hankali tsawon lokaci.

Da tsarin, jama’a na iya sayen gidaje da motoci da samun ilimi da kiwon lafiya ta hanyar bashi, inda za su biya daga baya.

Shugaba Tinubu na ganin ya kamata duk wani ɗan Najeriya ya samu damar more rayuwa ta tsarin karɓar bashi da zai taka rawa sosai wajen cimma wannan ƙudurin.

Tsarin wanda haɗin gwiwa ne tsakanin cibiyoyin hada-hadar kuɗi da ƙungiyoyin tsumi da tanadi a faɗin duniya, zai faɗaɗa damarmakin mai saye na samun kaya a kan bashi.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here