HomeLabarai‘Yan Bindiga sun kashe mutum 3 da sace 22 a Jihar Kaduna

‘Yan Bindiga sun kashe mutum 3 da sace 22 a Jihar Kaduna

Date:

Related stories

INEC ta ayyana 29 ga Maris a matsayin ranar zaben cike gurbi a Adamawa

Hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC), ta...

IPOB ta umarci ‘yan kabilar Igbo da ke Legas su koma gida

Kungiyar masu rajin kafa ‘yantacciyar kasar Biafara ta IPOB,...

Sarkin Kano ya taya Abba Kabir murnar lashe zaben gwamnan Kano

Sarkin Kano Aminu Ado Bayero ya taya Abba Kabir...

Mata magoya bayan PDP na zanga-zangar kin amincewa da zabe a Kaduna

Wata tawagar mata sanye da bakaken kaya na jam’iyyar...

‘Yan bindiga sun kashe mutane uku tare da yin garkuwa da wasu mutane 22 da suka hada da manoma a wasu kauyukan karamar hukumar Birnin-Gwari ta jihar Kaduna.

Shugaban kungiyar ci gaban masarautar Birnin-Gwari (BEPU), Ishaq Usman Kasai, wanda ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar, ya ce a ranar Asabar, 24 ga Satumba, 2022 da misalin karfe 7:30 na yamma, ‘yan bindigar sun kai hari Hayin Gada da ke unguwar Damari a gundumar Kazage, inda suka kashe mutum biyu wato; Sanusi Zubairu da Kabiru Zubairu da yni garkuwa da mutane 12 tare da wawashe kayan wasu shaguna a unguwar a yayin harin.

“A ranar Asabar din nan ne wasu ‘yan bindiga suka kashe mutum 1 tare da yin garkuwa da mutane 6 a FARM CENTER da ke kusa da titin Birnin-Gwari/Kaduna sun yi garkuwa da wasu 4 a Dajin Jangali tare da kwace babura 3 (Bajaj Model) na manoma a unguwar Kamfanin Doka.”

BEPU ya lura da tsananin damuwa da yadda ‘yan bindiga ke ci gaba da mamaye al’ummomi daban-daban da wawure kayayyaki a shaguna da fuskantar kalubale.

Shugaban kungiyar ta BEPU ya ce kungiyar ba za ta yi kasa a gwiwa ba wajen ci gaba da yin kira ga hukumomin da abin ya shafa da su kara kaimi wajen yakar ayyukan ta’addanci a karamar hukumar Birnin-Gwari musamman a wannan lokaci na noma.

 

LEADERSHIP

 

Subscribe

- Never miss a story with notifications

- Gain full access to our premium content

- Browse free from up to 5 devices at once

Latest stories