Kotu ta soke zaben fidda gwani na gwamnan APC a Adamawa

0
54

Wata babbar kotun tarayya da ke zamanta a Yola ta soke zaben fidda gwani na jam’iyyar All Progressives Congress (APC) wanda ya samar da Sanata Aishatu Binani a matsayin ‘yar takarar gwamnan jihar Adamawa a jam’iyyar.

Kotu a kan karar  da Mallam Nuhu Ribadu da ya shigar, kotu ta bayyana takarar Binani a matsayin mara amfani kuma haramun ne.

Mai shari’a Abdulaaziz Anka, a hukuncin da ya yanke, ya kuma ki amincewa da bukatar sake sake zaben fidda gwani, yana mai cewa jam’iyyar APC a hukuncin kotu ba ta da dan takarar gwamna a zaben 2023.

Alkalin ya yanke hukuncin ne bayan warware dukkan batutuwan da suka shafi sakamakon zaben fidda gwani na gwamnan jihar Adamawa da aka gudanar a ranar 26 ga Mayu, 2022.

A cewar sa, zaben fidda gwanin bai bi dokar zabe ta 2022 ba, da kundin tsarin mulkin kasa, da kuma ka’idojin jam’iyya.

Anka ya bayyana cewa nadin Sanata Aishatu Ahmed, wanda aka fi sani da Binani, ya sabawa sashe na 85 na dokar zabe, domin an yi tazarce.

Ya ce, “Binciken da na samu shi ne rashin bin dokar zabe, da kuma ka’idojin jam’iyya da tsarin mulki saboda an nuna cewa an yi sama-da-fadi, wanda aka tabbatar da babu shakka.

“Wanda ake kara na farko (APC) ba zai iya tsayar da dan takara a zaben 2023 ba; zaben fidda gwani ba shi da inganci, don haka kotu ta ga dawowar Aishatu Ahmed Binani a matsayin haramun.