HomeLabaraiYanke Albashi: ASUU ta kira taron gaggawa

Yanke Albashi: ASUU ta kira taron gaggawa

Date:

Related stories

INEC ta ayyana 29 ga Maris a matsayin ranar zaben cike gurbi a Adamawa

Hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC), ta...

IPOB ta umarci ‘yan kabilar Igbo da ke Legas su koma gida

Kungiyar masu rajin kafa ‘yantacciyar kasar Biafara ta IPOB,...

Sarkin Kano ya taya Abba Kabir murnar lashe zaben gwamnan Kano

Sarkin Kano Aminu Ado Bayero ya taya Abba Kabir...

Mata magoya bayan PDP na zanga-zangar kin amincewa da zabe a Kaduna

Wata tawagar mata sanye da bakaken kaya na jam’iyyar...

Kungiyar Malaman Jami’a (ASUU) ta kira zaman gaggawa na Majalisar Zartarwarta don yanke shawara kan shiga sabon yajin aiki.

ASUU ta kiran zaman gaggawan ne sakamakon rabin albashin watan Oktoba da Gwamnatin Tarayya ta biya malaman jami’a bayan sun janye yajin aiki.

Wani mamba a kwamitin zartarwar ASUU ya ce mambobin kungiyar sun fusata da yanke albashin nasu da suke zargin Ministan Kwadago, Chris Ngige ya yi.

Wani jami’in kungiyar ya shaida wa wakilinmu cewa majiya mai tushe ce ta sanar da su cewa ministan ne ya ba da umarnin yanke albashin da aka biya su a Oktoba.

“Ina tabbatar maka cewa NEC din ASUU NEC zai yi zama ranar Litinin 7 ga Nuwamba domin daukar matsaya game da shiga sabon yajin aiki, saboda rabin albashin da aka biya mu a Oktoba.

“Rassann kungiyar sun fusata da abin da Gwamnatin Tarayya ta yi, don haka kungiyar za ta yanke shawara a ranar 7 ga watan Nuwamba,” in ji shi ta wayar tarho.

Wakilimu ya yi kokarin samun shugaban kungiyar, Farfesa Emmanuel Osodeke domin sammun karin haske, sai dai wayarsa ba ta shiga.

Subscribe

- Never miss a story with notifications

- Gain full access to our premium content

- Browse free from up to 5 devices at once

Latest stories