HomeLabaraiBayan sauke daraktan NYSC, Christy za ta rike mukamin na wucin gadi

Bayan sauke daraktan NYSC, Christy za ta rike mukamin na wucin gadi

Date:

Related stories

INEC ta ce ba a kammala zabe a jihar Adamawa ba

Hukumar zaben Najeriya INEC, ta ayyana zaben gwamnan jihar...

An kashe ‘yan sanda 2, da dama sun raunata a wata arangama da sojoji a Taraba

A ranar Litin ne wasu sojoji suka kashe ‘yansanda...

Gwamna Zulum ya sake lashe zaben gwamna a jihar Borno

Sakamakon da hukumar zabe mai zaman kanta ta sanar...

Sojoji sun kashe hatsabinin dan ta’adda Umaru Nagona

Dakarun sojin Najeriya sun hallaka, Umaru Nagona, daya daga...

An kona gidan mawakin siyasa Rarara a Kano

Wasu da ake zargi ’yan daba ne sun banka...

Biyo bayan sauke Birgediya-Janar Muhammad Kaku Fadah daga mukaminsa na darakta janar na Hukumar Masu Yi Wa Kasa Hidima (NYSC), daraktar sashen Kimiyya da Fasaha, Christy Uba, za ta rike mukamin na wucin gadi.

A makon da ya wuce ne shugaban kasa Muhammadu Buhari, ya cire Fadah daga kan mukamin.

Buhari a ranar 17 ga watan Nuwambar 2022 ne, ya amince da a cire Fadah daga kan mukamin.

Rahotannin sun ce, shugaban ya bayar da umarnin a cire Fadah ne, saboda gazawarsa na iya tafiyar da hukumar.

A cikin wata sanarwar da kakakin hukumar ya fitar, ta ce ganin cewa, Christy ita ce babba yanzu a hukumar shi ya sa shugaban kasa ya amince da ta rike mukakin na wucin gadi kafin a nada wani sabon shugaban.

Subscribe

- Never miss a story with notifications

- Gain full access to our premium content

- Browse free from up to 5 devices at once

Latest stories