HomeLabaraiWasanniRonaldo ya ci kwallon sa na 500 a Saudiyya

Ronaldo ya ci kwallon sa na 500 a Saudiyya

Date:

Related stories

INEC ta ayyana 29 ga Maris a matsayin ranar zaben cike gurbi a Adamawa

Hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC), ta...

IPOB ta umarci ‘yan kabilar Igbo da ke Legas su koma gida

Kungiyar masu rajin kafa ‘yantacciyar kasar Biafara ta IPOB,...

Sarkin Kano ya taya Abba Kabir murnar lashe zaben gwamnan Kano

Sarkin Kano Aminu Ado Bayero ya taya Abba Kabir...

Mata magoya bayan PDP na zanga-zangar kin amincewa da zabe a Kaduna

Wata tawagar mata sanye da bakaken kaya na jam’iyyar...

Cristiano Ronaldo ya kafa tarihin zura kwallaye 500 a sabuwar kungiyarsa ta Al-Nassr da ke kasar Saudiyya.

Ronaldo ya zura kwallonsa na 500 ne a wasan da shi kadai ya ci kwallaye hudu a fafatawar da Al-Nassr ta casa kungiyar Al-Wehda 4-0 a Gasar Kwararru ta Kasar Saudiyya ranar Alhamis da dare.

Dan wasan ya zura kwallonsa na 500 a gasar kulob-kulob ne a minti na 21 ma wasan, inda ya yi murna da irin salon da ya saba.

Kwallonsa na 500 shi ne na biyu tun bayan dawowarsa Al-Nassr daga Manchester United; Daga bisani ya kara na 501, 502 da kuma 503 a ragar Al-Wehda.

A ranar Juma’a, 17 ga watan Fabrairu kuma, Al-Nassr za ta fafata da kungiyar Al-Taawoun a Gasar Zakarun Saudiyya da ke gudana.

Kawo yanzu Ronaldo dan kasar Portugal na da kwallaye 503 da ya ci a kungiyoyi biyar da ya taka wa leda a gasar kulob-kulob.

Ya ci 311 a zamansa a Real Madrid, 103 a lokuta daban-daban a Manchester United, 81 a kungiyar Juventus, uku a Sporting, sai kuma hudu a sabuwar kungiyarsa ta Al-Nassr.

A ranar Juma’a, 17 ga watan Fabrairu da muke ciki kuma Al-Nassr za ta fafata da kungiyar Al-Taawoun a Gasar Zakarun Saudiyya da ke gudana.

Subscribe

- Never miss a story with notifications

- Gain full access to our premium content

- Browse free from up to 5 devices at once

Latest stories

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here