‘Yan Najeriya na bayyana damuwa akan nade naden da Buhari keyi

0
76

Yayin da wasu mutane ke kallon matakin a matsayin wani tarko da gwamnatin ke ‘danawa wadanda zasu gaje su, zababben shugaban kasar Bola Ahmed Tinubu da kuma gwamnoni masu jiran gado, musamman wadanda suka fito jam’iyya guda da wadanda zasu gada, sun ki cewa uffan a bainar jama’a dangane da wadannan matakan da ake dauka.

Rahotanni daga matakin tarayya zuwa na jihohi na nuna yadda shugaban kasa Buhari ke ci gaba da nade nade da kuma amincewa da sabbin kwangiloli na miliyoyin nairori, yayin da suma gwamnonin jihohi ke bin wannan mataki, wanda ke samun goyan baya ko amincewar majalisar kasa da ta jihohin.

Daga cikin irin wadannan bukatu harda amincewar ciwo bashin dala miliyan 800 daga Bankin Duniya da majalisar kasa tayi domin rabawa talakawa a matsayin rage radadin cire tallafin man da gwamnati ta dakatar da aiwatarwa da kuma gabatar da bukatar biyan dala miliyan 556 da fam miliyan 98 da naira miliyan 226 a matsayin basussukan shari’ar da ake bin gwamnatin tarayya.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here