Pantami ya samu babbar lambar yabo ta “Award of Excellence”

0
62

Gidan Talabijin na Qausain ya ba tsohon Ministan Sadarwa da Tattalin Arziki na zamani, Farfesa Isa Pantami lambar yabo ta “Award of Excellence”.

Shugaban gidan talabijin din na kasa Malam Albanin Agege ne ya ba shi lambar yabon a Abuja.

Agege ya ce tsohon ministan ya cancanci lambar yabo ne saboda irin gudunmawar da ya bayar wajen bunkasa harkar sadarwa da tattalin arziki.

Ya kara da cewa, bisa la’akari da kyawawan manufofin da aka bullo da su a karkashin kulawar ma’aikatar, ya mayar da bangaren tattalin arziki na dijital a Najeriya kan turbar ci gaba mai dorewa.

Yayin da yake karbar lambar yabon, Pantami ya yabawa mahukuntan gidan rediyon bisa yadda suka fahimci nasarorin da ya samu a fannin.

Ya kuma yaba da kokarinsa na gidan talabijin na Qausain wajen samar da ingantattun bayanai da kuma samar da ayyuka masu kyau ga jama’a a Najeriya da ma sauran kasashen duniya.

Bikin ya samu halartar ‘yan uwa da abokan arziki da kuma tawagar ‘yan jarida da suka halarci taron.

NAN )

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here